< Zabura 95 >

1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
¡Vengan, cantemos con gozo a Yavé! ¡Aclamemos con júbilo a la Roca de nuestra salvación!
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Entremos ante su Presencia con acción de gracias, Aclamémoslo con salmos.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Porque Yavé es ʼEL grande, Y gran Rey sobre todos los ʼelohim.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
En su mano están las profundidades de la tierra. Suyas son las alturas de las montañas.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
Suyo es el mar, pues Él lo hizo, Y sus manos formaron la tierra seca.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Vengan, adoremos y postrémonos. Arrodillémonos [ante] la Presencia de Yavé, nuestro Hacedor,
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Porque Él es nuestro ʼElohim, Nosotros el pueblo de su prado y ovejas de su mano. Si ustedes oyen hoy su voz,
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
No endurezcan sus corazones como en Meriba, Como en el día de Masa en el desierto,
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
Cuando me tentaron sus antepasados. Me probaron, aunque vieron mi obra.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Durante 40 años estuve disgustado con aquella generación, Y dije: Es un pueblo que divaga en su corazón, Y no conoce mis caminos.
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Por tanto, juré en mi ira Que no entrarán en mi reposo.

< Zabura 95 >