< Zabura 95 >
1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Venid, alegrémonos para Yahvé; aclamemos a la Roca de nuestra salvación.
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Acerquémonos a Él con alabanzas, y con cantos gocémonos en su presencia.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Porque Yahvé es un gran Dios, y un rey más grande que todos los dioses.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
En sus manos están las profundidades de la tierra y son suyas las cumbres de las montañas.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
Suyo es el mar, pues Él lo hizo, y el continente, que plasmaron sus manos.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Venid, adoremos e inclinémonos; caigamos de rodillas ante Yahvé que nos creó.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Porque Él es nuestro Dios; nosotros somos el pueblo que Él alimenta, y las ovejas que Él cuida. Ojalá oyerais hoy aquella voz suya:
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
“No endurezcáis vuestros corazones como en Meribá, como en el día de Masá, en el desierto,
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
cuando vuestros padres me provocaron poniéndome a prueba aunque habían visto mis obras.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Durante cuarenta años me dio asco aquella generación y dije: “Son un pueblo de corazón extraviado, no han conocido mis caminos.”
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Por eso, indignado, juré: “No entrarán en mi reposo.”