< Zabura 95 >
1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
laus cantici David venite exultemus Domino iubilemus Deo salutari nostro
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
praeoccupemus faciem eius in confessione et in psalmis iubilemus ei
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
quoniam Deus magnus Dominus et rex magnus super omnes deos
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
quia in manu eius fines terrae et altitudines montium ipsius sunt
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
quoniam ipsius est mare et ipse fecit illud et siccam manus eius formaverunt
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
venite adoremus et procidamus et ploremus ante Dominum qui fecit nos
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
quia ipse est Deus noster et nos populus pascuae eius et oves manus eius
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
hodie si vocem eius audieritis nolite obdurare corda vestra
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
sicut in inritatione secundum diem temptationis in deserto ubi temptaverunt me patres vestri probaverunt me; et viderunt opera mea
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
quadraginta annis offensus fui generationi illi et dixi semper errant corde
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
et isti non cognoverunt vias meas ut iuravi in ira mea si intrabunt in requiem meam