< Zabura 95 >

1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
さあ、われらは主にむかって歌い、われらの救の岩にむかって喜ばしい声をあげよう。
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
われらは感謝をもって、み前に行き、主にむかい、さんびの歌をもって、喜ばしい声をあげよう。
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
主は大いなる神、すべての神にまさって大いなる王だからである。
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
地の深い所は主のみ手にあり、山々の頂もまた主のものである。
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
海は主のもの、主はこれを造られた。またそのみ手はかわいた地を造られた。
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
さあ、われらは拝み、ひれ伏し、われらの造り主、主のみ前にひざまずこう。
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
主はわれらの神であり、われらはその牧の民、そのみ手の羊である。どうか、あなたがたは、きょう、そのみ声を聞くように。
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
あなたがたは、メリバにいた時のように、また荒野のマッサにいた日のように、心をかたくなにしてはならない。
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
あの時、あなたがたの先祖たちはわたしのわざを見たにもかかわらず、わたしを試み、わたしをためした。
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
わたしは四十年の間、その代をきらって言った、「彼らは心の誤っている民であって、わたしの道を知らない」と。
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
それゆえ、わたしは憤って、彼らはわが安息に入ることができないと誓った。

< Zabura 95 >