< Zabura 95 >

1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Marilah kita menyanyi bagi TUHAN, bersorak-sorai bagi penyelamat kita!
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Mari kita menghadap Dia dengan lagu syukur, bersorak-sorak bagi-Nya dengan lagu pujian.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Sebab TUHAN adalah Allah yang agung, Raja perkasa yang mengatasi segala dewa.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
Ia menguasai bagian-bagian terdalam dari bumi, puncak-puncak gunung pun milik-Nya.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
Ia menguasai laut, sebab Dia yang membuatnya, daratan pun buah tangan-Nya.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Marilah kita sujud menyembah Dia, berlutut di hadapan TUHAN, pencipta kita.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Sebab Dialah Allah kita, kita umat yang dipelihara-Nya, seperti domba gembalaan-Nya. Pada hari ini dengarlah suara-Nya:
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
"Jangan keras kepala seperti leluhurmu di Meriba, seperti waktu mereka di Masa, di padang gurun.
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
Di sana mereka mencobai Aku, walaupun telah melihat perbuatan-Ku.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Empat puluh tahun lamanya Aku muak akan mereka; kata-Ku: Sungguh, bangsa itu tidak setia! Mereka tidak mengindahkan perintah-perintah-Ku
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Maka Aku bersumpah dalam kemarahan-Ku, mereka tak akan masuk ke negeri itu untuk mendapat istirahat bersama Aku."

< Zabura 95 >