< Zabura 95 >

1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Wohlan! Laßt uns dem Herrn zujauchzen, zujubeln unserm hilfereichen Hort!
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Laßt Uns mit Lobpreis vor sein Antlitz treten, mit Liedern ihm entgegenjauchzen!
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Der Herr ein großer Gott, Großkönig über alle Götter!
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
In seiner Hand der Erde Tiefen, sein sind der Berge Gipfel.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
Sein ist das Meer: Er hat's gemacht; das trockene Land: Er hat mit seinen Händen es gestaltet.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Herbei, anbetend laßt uns niederfallen und niederknieen vor dem Herrn und unserm Schöpfer!
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Er ist alleinig unser Gott, und wir sein Weidevolk und seine liebste Herde, wenn ihr auf seine Stimme heute horcht:
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
"Verhärtet euer Herz nicht, wie zu Meriba, wie in der Wüste am Versuchungstag,
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
wo eure Väter mich versucht und mich geprüft, obschon sie meine Tat gesehen.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Ich grollte vierzig Jahre dem Geschlechte; ich sprach: Es ist ein Volk mit einem irren Geist; sie achten nicht auf meine Wege.
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Ich schwur daher in meinem Zorn: Nie gehen sie zu meiner Ruhstätte ein!"

< Zabura 95 >