< Zabura 95 >
1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Kommet, lasset uns Jehova zujubeln, lasset uns zujauchzen dem Felsen unseres Heils!
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Lasset uns ihm entgegengehen mit Lob, lasset uns mit Psalmen ihm zujauchzen!
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Denn ein großer Gott ist Jehova, und ein großer König über alle Götter;
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
in dessen Hand die Tiefen der Erde, und dessen die Höhen der Berge sind;
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
dessen das Meer ist, er hat es ja gemacht; und das Trockene, seine Hände haben es gebildet.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Kommet, lasset uns anbeten und uns niederbeugen, lasset uns niederknien vor Jehova, der uns gemacht hat!
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Denn er ist unser Gott, und wir sind das Volk seiner Weide und die Herde seiner Hand. Heute, wenn ihr seine Stimme höret,
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
verhärtet euer Herz nicht, wie zu Meriba, wie am Tage von Massa in der Wüste;
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
als eure Väter mich versuchten, mich prüften, und sie sahen doch mein Werk!
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Vierzig Jahre hatte ich Ekel an dem Geschlecht, und ich sprach: Ein Volk irrenden Herzens sind sie. Aber sie haben meine Wege nicht erkannt;
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
so daß ich schwur in meinem Zorn: Wenn sie in meine Ruhe eingehen werden!