< Zabura 95 >
1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Venez, chantons à l'Éternel; jetons des cris de joie au rocher de notre salut.
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Présentons-nous à lui avec des louanges; offrons-lui nos joyeux cantiques.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Car l'Éternel est un Dieu grand, il est un grand roi au-dessus de tous les dieux.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
C'est en sa main que sont les abîmes de la terre; à lui sont les sommets des montagnes.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
A lui appartient la mer, car il l'a faite, et ses mains ont formé la terre.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Venez, prosternons-nous, inclinons-nous; fléchissons les genoux devant l'Éternel qui nous a faits.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Car il est notre Dieu, nous sommes le peuple qu'il fait paître et les brebis qu'il conduit.
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
Aujourd'hui, si vous entendez sa voix, n'endurcissez pas votre cœur comme à Mériba (Querelle), comme au jour de Massa (Tentation), dans le désert,
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
Où vos pères m'ont tenté et m'ont éprouvé, où ils ont aussi vu mes œuvres.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Pendant quarante ans j'eus cette génération en dégoût, et je dis: C'est un peuple dont le cœur s'égare; ils n'ont point connu mes voies.
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Aussi je l'ai juré dans ma colère: S'ils entrent dans mon repos!