< Zabura 95 >

1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Venez, chantons à l'Eternel, jetons des cris de réjouissance au rocher de notre salut.
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Allons au-devant de lui en lui présentant nos louanges; et jetons devant lui des cris de réjouissance en chantant des Psaumes.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Car l'Eternel est un [Dieu] Fort[et] grand, et il est un grand Roi par-dessus tous les dieux.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
Les lieux les plus profonds de la terre sont en sa main, et les sommets des montagnes sont à lui.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
C'est à lui qu'appartient la mer, car lui-même l'a faite, et ses mains ont formé le sec.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Venez, prosternons-nous, inclinons-nous, et mettons-nous à genoux devant l'Eternel qui nous a faits.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Car il est notre Dieu, et nous sommes le peuple de sa pâture, et les brebis de sa conduite. Si vous entendez aujourd'hui sa voix,
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
N'endurcissez point votre cœur, comme en Mériba, [et] comme à la journée de Massa, au désert;
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
Là où vos pères m'ont tenté et éprouvé; et aussi ont-ils vu mes œuvres.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
J'ai été ennuyé de cette génération durant quarante ans, et j'ai dit: c'est un peuple dont le cœur s'égare; et ils n'ont point connu mes voies;
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
C'est pourquoi j'ai juré en ma colère, s'ils entrent dans mon repos.

< Zabura 95 >