< Zabura 95 >
1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Cantique de louange, de David. Venez, réjouissons-nous dans le Seigneur; poussons des cris de joie vers Dieu, notre Sauveur.
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Présentons-nous devant sa face pour lui rendre grâces, et chantons-lui des psaumes avec allégresse.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Car c'est un grand Dieu que le Seigneur, et un roi plus grand que tous les dieux.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
Le Seigneur ne répudiera point son peuple; il tient en sa main les confins de la terre, et les cimes des monts sont à lui.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
Car la mer est sienne, c'est lui qui l'a faite, et ses mains ont formé la terre ferme.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Venez, prosternons-nous devant lui pour l'adorer; et pleurons devant le Seigneur qui nous a faits.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Car il est notre Dieu, et nous, nous sommes le peuple de son pâturage et les brebis de sa main.
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
Aujourd'hui, si vous entendez sa voix, n'endurcissez pas vos cœurs, comme au jour de la colère et de la tentation dans le désert.
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
Lorsque vos pères m'ont tenté, ils m'ont éprouvé, et ils ont vu mes œuvres.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Pendant quarante ans, j'ai conservé ma colère contre cette génération, et j'ai dit: Ils s'égarent toujours en leur cœur!
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Et ils n'ont point connu mes voies. C'est pourquoi, en ma colère, j'ai juré qu'ils n'entreraient pas en mon repos.