< Zabura 95 >

1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
O come, let us sing to the LORD: let us make a joyful noise to the rock of our salvation.
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Let us come before his presence with thanksgiving, and make a joyful noise to him with psalms.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
For the LORD [is] a great God, and a great King above all gods.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
In his hand [are] the deep places of the earth: the strength of the hills [is] his also.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
The sea [is] his, and he made it: and his hands formed the dry [land].
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
O come, let us worship and bow down: let us kneel before the LORD our maker.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
For he [is] our God; and we [are] the people of his pasture, and the sheep of his hand. To-day, if ye will hear his voice,
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
Harden not your heart, as in the provocation, [and] as [in] the day of temptation in the wilderness:
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
When your fathers tempted me, proved me, and saw my work.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Forty years long was I grieved with [this] generation, and said, It [is] a people that do err in their heart, and they have not known my ways:
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
To whom I swore in my wrath, that they should not enter into my rest.

< Zabura 95 >