< Zabura 95 >
1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Come, let vs reioyce vnto the Lord: let vs sing aloude vnto the rocke of our saluation.
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Let vs come before his face with praise: let vs sing loude vnto him with Psalmes.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
For the Lord is a great God, and a great King aboue all gods.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
In whose hande are the deepe places of the earth, and the heightes of the mountaines are his:
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
To whome the Sea belongeth: for hee made it, and his handes formed the dry land.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Come, let vs worship and fall downe, and kneele before the Lord our maker.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
For he is our God, and we are the people of his pasture, and the sheepe of his hande: to day, if ye will heare his voyce,
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
Harden not your heart, as in Meribah, and as in the day of Massah in the wildernesse.
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
Where your fathers tempted me, proued me, though they had seene my worke.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Fourtie yeeres haue I contended with this generation, and said, They are a people that erre in heart, for they haue not knowen my wayes.
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Wherefore I sware in my wrath, saying, Surely they shall not enter into my rest.