< Zabura 95 >
1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
O come, let us sing to Jehovah. Let us make a joyful noise to the rock of our salvation.
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Let us come before his presence with thanksgiving. Let us make a joyful noise to him with psalms.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
For Jehovah is a great God, and a great King above all gods.
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
In his hand are the deep places of the earth. The heights of the mountains are also his.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
The sea is his, and he made it. And his hands formed the dry land.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
O come, let us worship and bow down. Let us kneel before Jehovah our maker.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
For he is our God, and we are the people of his pasture, and the sheep of his hand. Today, O that ye would hear his voice!
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
Harden not your heart, as in the provocation, as the day of trial in the wilderness,
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
where your fathers challenged me, proved me, and saw my work.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Forty years long I was grieved with that generation, and said, It is a people that do err in their heart, and they have not known my ways.
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Therefore I swore in my wrath that they should not enter into my rest.