< Zabura 95 >

1 Ku zo, bari mu rera don farin ciki ga Ubangiji; bari mu yi sowa da ƙarfi ga Dutsen cetonmu.
Poďte, zpívejme Hospodinu, prokřikujme skále spasení našeho.
2 Bari mu zo gabansa da godiya mu rera gare shi da kiɗi da waƙa.
Předejděme oblíčej jeho s díkčiněním, žalmy prozpěvujme jemu.
3 Gama Ubangiji Allah mai girma ne, babban Sarki a bisa dukan alloli.
Nebo Hospodin jest Bůh veliký, a král veliký nade všecky bohy,
4 A hannunsa ne zurfafan duniya suke, ƙwanƙolin dutse kuma nasa ne.
V jehož rukou základové země, a vrchové hor jeho jsou.
5 Teku nasa ne, gama shi ne ya yi shi, da hannuwansa kuma ya yi busasshiyar ƙasa.
Jehož jest i moře, nebo on je učinil, i země, kterouž ruce jeho sformovaly.
6 Ku zo, bari mu rusuna mu yi sujada, bari mu durƙusa a gaban Ubangiji Mahaliccinmu;
Poďte, sklánějme se, a padněme před ním, klekejme před Hospodinem stvořitelem naším.
7 gama shi ne Allahnmu mu mutanen makiyayansa ne, garke kuwa a ƙarƙashin kulawarsa. Yau, in kuka ji muryarsa,
Onť jest zajisté Bůh náš, a my jsme lid pastvy jeho, a stádo rukou jeho. Dnes uslyšíte-li hlas jeho,
8 “Kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a Meriba, kamar yadda kuka yi a wancan rana a Massa a hamada,
Nezatvrzujte srdce svého, jako při popuzení, a v den pokušení na poušti,
9 inda kakanninku suka gwada suka kuma jarraba ni, ko da yake sun ga abin da na yi.
Kdežto pokoušeli mne otcové vaši, zkusiliť jsou mne, a viděli skutky mé.
10 Shekara arba’in na yi fushi da wancan tsara; na ce, ‘Su mutane ne waɗanda zukatansu suka kauce, kuma ba su san hanyoyina ba.’
Za čtyřidceti let měl jsem nesnáz s národem tím, a řekl jsem: Lid tento bloudí srdcem, a nepoznali cest mých.
11 Saboda haka na yi rantsuwa cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
Jimž jsem přisáhl v hněvě svém, že nevejdou v odpočinutí mé.

< Zabura 95 >