< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Du hämndens Gud, o HERRE, du hämndens Gud, träd fram i glans.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Res dig, du jordens domare, vedergäll de högmodiga vad de hava gjort.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Huru länge skola de ogudaktiga, o HERRE, huru länge skola de ogudaktiga triumfera?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Deras mun flödar över av fräckt tal; de förhäva sig, alla ogärningsmännen.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Ditt folk, o HERRE, krossa de, och din arvedel förtrycka de.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Änkor och främlingar dräpa de, och faderlösa mörda de.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Och de säga: "HERREN ser det icke, Jakobs Gud märker det icke."
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Märken själva, I oförnuftiga bland folket; I dårar, när kommen I till förstånd?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Den som har planterat örat, skulle han icke höra? Den som har danat ögat, skulle han icke se?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Den som håller hedningarna i tukt, skulle han icke straffa, han som lär människorna förstånd?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
HERREN känner människornas tankar, han vet att de själva äro fåfänglighet.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Säll är den man som du, HERRE, undervisar, och som du lär genom din lag,
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
för att skaffa honom ro för olyckans dagar, till dess de ogudaktigas grav varder grävd.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Ty HERREN förskjuter icke sitt folk, och sin arvedel övergiver han icke.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Nej, rättfärdighet skall åter gälla i rätten, och alla rättsinniga skola hålla sig därtill.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Vem står upp till att försvara mig mot de onda, vem bistår mig mot ogärningsmännen?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Om HERREN icke vore min hjälp, så bodde min själ snart i det tysta.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
När jag tänkte: "Min fot vacklar", då stödde mig din når, o HERRE:
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
När jag hade mycket bekymmer i mitt hjärta, då gladde din tröst min själ.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Kan fördärvets domarsäte hava gemenskap med dig, det säte där man över våld i lagens namn,
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
där de tränga den rättfärdiges själ och fördöma oskyldigt blod?
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Men HERREN bliver för mig en borg, min Gud bliver min tillflykts klippa.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Och han låter deras fördärv vända tillbaka över dem och förgör dem för deras ondskas skull. Ja, HERREN, vår Gud, förgör dem.

< Zabura 94 >