< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Yahwe, Ee Mungu ulipaye kisasi, Mungu ulipaye kisasi, utuangazie sisi.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Inuka, muhukumu wa nchi, uwape wenye majivuno kile wanachosahili.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Mpaka lini waovu, Yahwe, mpaka lini waovu watafurahia?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Wanamwaga maneno yao ya kiburi; wote watendao uovu wanajivuna.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Wanawaangamiza watu wako, Yahwe; wanalitesa taifa ambao ni milki yako.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Wanamuua mjane na mgeni aishiye nchini mwao, na wanamuua yatima.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Nao husema, “Yahwe hawezi kuona, Mungu wa Yakobo hayagundui haya.”
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Tambueni, ninyi watu wajinga! Enyi wapumbavu, mtajifunza lini?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Yeye aliye liumba sikio, hasikii? Yeye aliye litengeneza jicho, haoni?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Yeye awaadhibuye mataifa, hayuko sahihi? Yeye ndiye ampaye maarifa mwanadamu.
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Yahwe anayajua mawazo ya wanadamu, kuwa ni mvuke.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Amebarikiwa yule ambaye umuongozaye, Yahwe, yule ambaye wewe humfundisha kutoka katika sheria yako.
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
Wewe humpa pumziko wakati wa shida mpaka shimo litakapokuwa limechimbwa kwa ajili ya waovu.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Maana Yahwe hatawaacha watu wake wala kutelekeza warithi wake.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Kwa kuwa tena hukumu itakuwa ya haki; na wote walio wanyoofu wa moyo wataifuata.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Ni nani atainuka kunitetea dhidi ya watendao uovu? Ni nani atasimama dhidi ya waovu kwa ajili yangu?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Kama Yahwe asingelikuwa msaada wangu, haraka ningekuwa nimelala mahali pa ukimya.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Niliposema, mguu wangu unateleza,” Uaminifu wa agano lako, Yahwe, uliniinua.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Wasiwasi uwapo mwingi ndani yangu, faraja yako hunifurahisha.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Kiti cha uharibifu chaweza kushirikiana nawe, kitungacho madhara kwa njia ya sheria?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Wao kwa pamoja hupanga njama kuwaua wenye haki na kuwahukumu adhabu ya kifo wenye haki.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Lakini Yahwe amekuwa mnara wangu mrefu, na Mungu wangu amekuwa mwamba wa kimbilio langu.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Yeye atawarudishia uovu wao wenyewe na atawaangamiza katika uovu wao wenyewe. Yahwe Mungu wetu atawaangamiza.

< Zabura 94 >