< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Ee Bwana, ulipizaye kisasi, Ee Mungu ulipizaye kisasi, uangaze sasa.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Ee Mhukumu wa dunia, inuka, uwalipize wenye kiburi kama wanavyostahili.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Hata lini, waovu, Ee Bwana, hata lini waovu watashangilia?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Wanamimina maneno ya kiburi, watenda mabaya wote wamejaa majivuno.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Ee Bwana, wanawaponda watu wako, wanawaonea urithi wako.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Wanamchinja mjane na mgeni, na kuwaua yatima.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Nao husema, “Bwana haoni, Mungu wa Yakobo hafahamu.”
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Sikizeni, enyi wajinga miongoni mwa watu; enyi wapumbavu, lini mtakuwa na hekima?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Je, aliyeweka sikio asisikie? Aliyeumba jicho asione?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Je, anayeadhibisha mataifa asiadhibu? Je, awafundishaye wanadamu asiwe na maarifa?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Bwana anajua mawazo ya mwanadamu; anajua kwamba ni ubatili.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Ee Bwana, heri mtu anayeadhibishwa na wewe, mtu unayemfundisha kwa sheria yako,
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
unampa utulivu siku za shida, mpaka shimo litakapokuwa limechimbwa kwa ajili ya mwovu.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Kwa kuwa Bwana hatawakataa watu wake, hatauacha urithi wake.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Hukumu itasimamishwa tena kwenye haki, wote walio na mioyo minyofu wataifuata.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Ni nani atakayeinuka dhidi ya mwovu kwa ajili yangu? Ni nani atakayenikinga dhidi ya watenda maovu?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Kama Bwana asingelinisaidia upesi, ningelikuwa ninaishi katika ukimya wa kifo.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Niliposema, “Mguu wangu unateleza,” Ee Bwana, upendo wako ulinishikilia.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Wakati wasiwasi ulipokuwa mwingi ndani yangu, faraja yako ilinipa furaha nafsini mwangu.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Je, kiti cha utawala wa udhalimu kitajiunga nawe, ule utawala uletao taabu kutokana na sheria zake?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Huungana kuwashambulia wenye haki, kuwahukumu kufa wasio na hatia.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Lakini Bwana amekuwa ngome yangu, na Mungu wangu amekuwa mwamba ninaoukimbilia.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Yeye atawalipa kwa ajili ya dhambi zao na atawaangamiza kwa ajili ya maovu yao; Bwana Mungu wetu atawaangamiza.

< Zabura 94 >