< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
JEHOVÁ, Dios de las venganzas, Dios de las venganzas, muéstrate.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Ensálzate, oh Juez de la tierra: da el pago á los soberbios.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
¿Hasta cuándo los impíos, hasta cuándo, oh Jehová, se gozarán los impíos?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
¿Hasta cuándo pronunciarán, hablarán cosas duras, y se vanagloriarán todos los que obran iniquidad?
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
A tu pueblo, oh Jehová, quebrantan, y á tu heredad afligen.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
A la viuda y al extanjero matan, y á los huérfanos quitan la vida.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Y dijeron: No verá JAH, ni entenderá el Dios de Jacob.
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Entended, necios del pueblo; y vosotros fatuos, ¿cuándo seréis sabios?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
El que plantó el oído, ¿no oirá? el que formó el ojo, ¿no verá?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
El que castiga las gentes, ¿no reprenderá? ¿no sabrá el que enseña al hombre la ciencia?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Jehová conoce los pensamientos de los hombres, que son vanidad.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Bienaventurado el hombre á quien tú, JAH, castigares, y en tu ley lo instruyeres;
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
Para tranquilizarle en los días de aflicción, en tanto que para el impío se cava el hoyo.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Porque no dejará Jehová su pueblo, ni desamparará su heredad;
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Sino que el juicio será vuelto á justicia, y en pos de ella irán todos los rectos de corazón.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
¿Quién se levantará por mí contra los malignos? ¿quién estará por mí contra los que obran iniquidad?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Si no me ayudara Jehová, presto morara mi alma en el silencio.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Cuando yo decía: Mi pie resbala: tu misericordia, oh Jehová, me sustentaba.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
En la multitud de mis pensamientos dentro de mí, tus consolaciones alegraban mi alma.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
¿Juntaráse contigo el trono de iniquidades, que forma agravio en el mandamiento?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Pónense en corros contra la vida del justo, y condenan la sangre inocente.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Mas Jehová me ha sido por refugio; y mi Dios por roca de mi confianza.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Y él hará tornar sobre ellos su iniquidad, y los destruirá por su propia maldad; los talará Jehová nuestro Dios.

< Zabura 94 >