< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Oh Gospod Bog, ki mu pripada maščevanje, oh Bog, ki mu pripada maščevanje, pokaži se.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Dvigni se, ti sodnik zemlje; povrni nagrado ponosnim.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Gospod, doklej bodo zlobni, doklej bodo zlobni slavili zmago?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Kako dolgo bodo izgovarjali in govorili trde stvari in se bahali vsi delavci krivičnosti?
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Tvoje ljudstvo razbijajo na koščke, oh Gospod in prizadevajo tvojo dediščino.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Ubijajo vdovo in tujca in morijo osirotele.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Vendar pravijo: » Gospod nas ne bo videl niti Bog Jakobov tega ne bo upošteval.«
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Razumite, vi brutalni izmed ljudstva, in vi bedaki, kdaj boste modri?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Kdor je zasadil uho, da ne bi slišal? Kdor je oblikoval oko, da ne bi videl?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Kdor kaznuje pogane, da ne bi grajal? Kdor uči človeka spoznanja, da ne bi vedel?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Gospod pozna človekove misli, da so le-te ničevost.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Blagoslovljen je človek, ki ga karaš, oh Gospod in ga učiš iz svoje postave,
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
da mu lahko daš počitek od dni nadloge, dokler ni izkopana jama za zlobnega.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Kajti Gospod ne bo zavrgel svojega ljudstva niti ne bo zapustil svoje dediščine.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Toda sodba se bo vrnila k pravičnosti in vsi iskreni v srcu ji bodo sledili.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Kdo se bo zame dvignil zoper hudodelce? Ali kdo bo zame vstal zoper delavce krivičnosti?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Če Gospod ne bi bil moja pomoč, bi moja duša skoraj prebivala v tišini.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Ko sem rekel: »Moje stopalo zdrsuje, me je podpiralo tvoje usmiljenje, oh Gospod.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
V množici mojih misli znotraj mene tvoje tolažbe razveseljujejo mojo dušo.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Mar bo prestol krivičnosti, ki z uzakonitvijo snuje vragolijo, imel družbo s teboj?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Skupaj se zbirajo zoper dušo pravičnega in obsojajo nedolžno kri.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Toda Gospod je moja obramba in moj Bog je skala mojega zatočišča.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Nadnje bo privedel njihovo lastno krivičnost in odsekal jih bo v njihovi lastni zlobnosti; da, Gospod, naš Bog, jih bo odsekal.

< Zabura 94 >