< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Боже од освете, Господе, Боже од освете, покажи се!
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Подигни се, судијо земаљски, подај заслугу охолима.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Докле ће се безбожници, Господе, докле ће се безбожници хвалити?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Руже и охоло говоре, величају се сви који чине безакоње.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Газе народ Твој, Господе, и достојање Твоје муче.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Удовицу и дошљака убијају, и сироте море.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
И говоре: Неће видети Господ, и неће дознати Бог Јаковљев.
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Оразумите се, прелуди људи! Будале! Кад ћете бити паметни?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Који је створио ухо, зар не чује? И који је око начинио, зар не види?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Зар неће обличити који народе уразумљује, који учи човека да зна?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Господ зна мисли људима како су ништаве.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Благо човеку кога Ти, Господе, уразумљујеш, и законом својим учиш;
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
Да би му дао мир у зле дане, док се ископа јама безбожнику.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Јер неће одбацити Господ народ свој, и достојање своје неће оставити.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Јер ће се суд вратити на правду, у њега ће наћи сви правог срца.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Ко ће устати за мене супрот злима? Ко ће стати за мене супрот онима који чине безакоње?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Кад ми Господ не би био помоћник, брзо би се душа моја преселила онамо где се ћути.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Кад кажем: Дрхће ми нога, милост Твоја, Господе, прихвата ме.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Кад се умноже бриге у срцу мом, утехе Твоје разговарају душу моју.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Еда ли ће се близу Тебе стати престо крвнички, и онај који намишља насиље насупрот закону?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Спремају се на душу праведникову, и крв праву окривљују.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Али је Господ моје пристаниште, и Бог је мој тврдо уточиште моје.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Он ће им вратити за безакоње њихово, за њихову злоћу истребиће их, истребиће их Господ, Бог наш.

< Zabura 94 >