< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Oh Thixo, uNkulunkulu ophindiselayo, Oh Nkulunkulu ophindiselayo, khanya uvele.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Phakama, awu Mahluli womhlaba; baphindisele abazigqajayo ngokubafaneleyo.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Koze kube nini ababi, Oh Thixo, koze kube nini ababi beklamasa na?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Bathulula amazwi okukloloda; zonke izigangi zifuthelene ngokuzikhukhumeza.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Ziyabanyathezela abantu bakho, Oh Thixo; zincindezela ilifa lakho.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Zibulala umfelokazi kanye lowezizweni; zibulala intandane.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Zithi, “UThixo kaboni; uNkulunkulu kaJakhobe kananzi.”
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Limukani, lina elingelangqondo phakathi kwabantu; lina ziphukuphuku, lizahlakanipha nini?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Yena lowo owayigxumekayo indlebe kezwa yini? Yena lowo owabumba ilihlo kaboni na?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Yena lowo oqondisa izizwe kajezisi yini? Yena lowo ofundisa umuntu kalalwazi na?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
UThixo uyayazi imicabango yomuntu; uyayazi ukuthi iyize nje.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Ubusisiwe umuntu omqondisayo, Oh Thixo, umuntu omfundisa okomthetho wakho;
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
uyamphumuza ensukwini zokuhlupheka, kuze kuthi ababi bembelwe igodi.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Ngoba uThixo kazukwala abantu bakhe; kasoze lanini afulathele ilifa lakhe.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Ukwahlulela kuzaphinda njalo kumiswe ngokulunga, kuthi bonke abaqotho ngenhliziyo bakulandele.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Ngubani ozangimela ekulweni lababi na? Ngubani ozangelekelela ekulweni lezigangi na?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Aluba uThixo wayengangelulekanga, ngabe ngahle ngahlala ngathula zwi ekufeni.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Lapho ngasengisithi, “Unyawo lwami selutshelela,” uthando lwakho, Oh Thixo, lwangisekela.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Nxa ukunqineka kwase kungikhulela, induduzo yakho yaletha intokozo emphefumulweni wami.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Kambe isihlalo sobukhosi esixhwalileyo singema lawe yini leso esiletha inhlupheko ngezimemezelo zaso?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Bayahlangana ukumelana labalungileyo ongelacala agwetshelwe ukufa.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Kodwa uThixo useyinqaba yami, loNkulunkulu wami ulidwala engiphephela kulo.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Uzabaphindisela ngenxa yezono zabo ababhubhise ngenxa yobubi babo; uThixo uNkulunkulu wethu uzababhubhisa.

< Zabura 94 >