< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Psalmus ipsi David, Quarta Sabbati. Deus ultionum Dominus: Deus ultionum libere egit.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Exaltare qui iudicas terram: redde retributionem superbis.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Usquequo peccatores Domine: usquequo peccatores gloriabuntur:
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Effabuntur, et loquentur iniquitatem: loquentur omnes, qui operantur iniustitiam?
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Populum tuum Domine humiliaverunt: et hereditatem tuam vexaverunt.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Viduam, et advenam interfecerunt: et pupillos occiderunt.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Et dixerunt: Non videbit Dominus, nec intelliget Deus Iacob.
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Intelligite insipientes in populo: et stulti aliquando sapite.
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Qui plantavit aurem, non audiet? aut qui finxit oculum, non considerat?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Qui corripit gentes, non arguet: qui docet hominem scientiam?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Dominus scit cogitationes hominum, quoniam vanæ sunt.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Beatus homo, quem tu erudieris Domine: et de lege tua docueris eum.
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
Ut mitiges ei a diebus malis: donec fodiatur peccatori fovea.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Quia non repellet Dominus plebem suam: et hereditatem suam non derelinquet.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Quoadusque iustitia convertatur in iudicium: et qui iuxta illam omnes qui recto sunt corde.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Quis consurget mihi adversus malignantes? aut quis stabit mecum adversus operantes iniquitatem?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Nisi quia Dominus adiuvit me: paulominus habitasset in inferno anima mea. (questioned)
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Si dicebam: Motus est pes meus: misericordia tua Domine adiuvabat me.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Secundum multitudinem dolorum meorum in corde meo: consolationes tuæ lætificaverunt animam meam.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Numquid adhæret tibi sedes iniquitatis: qui fingis laborem in præcepto?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Captabunt in animam iusti: et sanguinem innocentem condemnabunt.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Et factus est mihi Dominus in refugium: et Deus meus in adiutorium spei meæ.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Et reddet illis iniquitatem ipsorum: et in malitia eorum disperdet eos: disperdet illos Dominus Deus noster.

< Zabura 94 >