< Zabura 94 >
1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
ヱホバよ仇をかへすは汝にあり神よあたを報すはなんぢにあり ねがはくは光をはなちたまへ
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
世をさばきたまふものよ 願くは起てたかぶる者にそのうくべき報をなしたまへ
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
ヱホバよ惡きもの幾何のときを經んとするや あしきもの勝誇りていくそのとしを經るや
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
かれらはみだりに言をいだして誇りものいふ すべて不義をおこなふ者はみづから高ぶれり
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
ヱホバよ彼等はなんぢの民をうちくだき なんぢの業をそこなふ
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
かれらは嫠婦と旅人との生命をうしなひ孤子をころす
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
かれらはいふ ヤハは見ずヤコブの神はさとらざるべしと
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
民のなかなる無知よ なんぢらさとれ 愚かなる者よ いづれのときにか智からん
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
みみを植るものきくことをせざらんや 目をつくれるもの見ることをせざらんや
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
もろもろの國ををしふる者ただすことを爲ざらんや 人に知識をあたふる者しることなからんや
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
ヱホバは人の思念のむなしきを知りたまふ
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
ヤハよなんぢの懲めたまふ人なんぢの法ををしへらるる人は さいはひなるかな
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
かかる人をわざはひの日よりのがれしめ 惡きもののために坑のほらるるまで これに平安をあたへたまはん
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
そはヱホバその民をすてたまはず その嗣業をはなれたまはざるなり
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
審判はただしきにかへり心のなほき者はみなその後にしたがはん
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
誰かわがために起りたちて惡きものを責んや 誰か我がために立て不義をおこなふ者をせめんや
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
もしヱホバ我をたすけたまはざりせば わが霊魂はとくに幽寂ところに住ひしならん
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
されどわが足すべりぬといひしとき ヱホバよなんぢの憐憫われをささへたまへり
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
わがうちに憂慮のみつる時 なんぢの安慰わがたましひを喜ばせたまふ
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
律法をもて害ふことをはかる惡の位はなんぢに親むことを得んや
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
彼等はあひかたらひて義人のたましひをせめ罪なき血をつみに定む
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
然はあれどヱホバはわがたかき櫓 わが神はわが避所の磐なりき
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
神はかれらの邪曲をその身におはしめ かれらをその惡き事のなかに滅したまはん われらの神ヱホバはこれを滅したまはん