< Zabura 94 >
1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Ya Allah, Engkaulah Allah yang membalas, tunjukkanlah pembalasan-Mu, ya TUHAN.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Bangkitlah, ya Hakim seluruh bumi, hukumlah orang congkak setimpal perbuatan mereka.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Ya TUHAN, sampai kapan orang jahat bergembira? Sampai kapan, ya TUHAN?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Mereka melontarkan kata-kata yang kasar, dan menyombongkan kejahatan mereka.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Mereka menindas umat-Mu, ya TUHAN, dan meremukkan orang-orang pilihan-Mu.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Mereka membunuh janda dan yatim piatu dan orang asing yang tinggal di negeri ini.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Kata mereka, "TUHAN tidak melihatnya, Allah Yakub tidak memperhatikannya."
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Hai bangsaku, janganlah sebodoh itu, belajarlah memakai akalmu!
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Allah yang membuat telinga, apakah Ia tidak mendengar? Dia yang membuat mata, apakah Ia tidak melihat?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Dia yang mengajar bangsa-bangsa, apakah Ia tidak menghukum? Dia yang menjadi guru semua orang, apakah Ia tidak mempunyai pengetahuan?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
TUHAN menyelami pikiran manusia, Ia tahu semuanya sia-sia belaka.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Berbahagialah orang yang Kaudidik, ya TUHAN, orang yang Kauajari hukum-hukum-Mu.
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
Kautenangkan dia di hari-hari malapetaka, sampai digali lubang untuk menangkap orang jahat.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Sebab TUHAN tak akan meninggalkan umat-Nya; Ia tak akan mengabaikan milik pusaka-Nya.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Maka hukum akan ditegakkan lagi di pengadilan, semua orang jujur akan mendukungnya.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Siapa membela aku terhadap orang durhaka? Siapa memihak aku melawan orang yang berbuat jahat?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Sekiranya TUHAN tidak menolong aku, aku nyaris pindah ke dunia orang mati.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Waktu aku berpikir bahwa aku akan jatuh, kasih-Mu, TUHAN, membuat aku berdiri kukuh.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Apabila hatiku cemas dan gelisah, Engkau menghibur dan menggembirakan aku.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Engkau tidak bersekutu dengan hakim-hakim jahat, yang merancangkan kejahatan berdasarkan hukum.
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Mereka bersekongkol melawan orang jujur, dan menghukum mati orang yang tak bersalah.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Tetapi TUHAN adalah pembelaku, Allahku menjadi pelindungku.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Ia menghukum orang jahat setimpal kejahatannya, dan membungkamkan mereka karena dosanya. TUHAN Allah kita akan membungkamkan mereka.