< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
O Yahweh, Dios a mangibales, Dios a mangibales, raniagannakami.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Tumakderka, ukom ti daga, itedmo kadagiti natangsit dagiti maiparbeng kadakuada.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
O Yahweh, kasano pay kabayag dagiti nadangkes, kasano pay kabayag iti panagragsak dagiti nadangkes?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Agisawsawangda kadagiti natangsit ken nakarit a panagsasao, ken naparammagda amin.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Ibaddebaddekda dagiti tattaom, O Yahweh; idadanesda ti nasionmo.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Pappapatayenda ti balo a babbai ken ti gangannaet, ken papatayenda dagiti ulila kadagiti ammada.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Kunada, “Saanto a makita ni Yaweh, saan a pagan-ano daytoy ti Dios ni Jacob.”
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Awatenyo, dakayo a nakuneng a tattao, dakayo a maag, kaano kayo pay a makasursuro? Isuna a nangaramid ti lapayag, saanna kadi a mangngeg?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Isuna a nangaramid ti mata, saanna kadi a makita?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Isuna a mangisursuro kadagiti nasion, saan kadi isuna a mangilinteg? Isuna ti mangmangted iti pannakaammo ti tao.
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Ammo ni Yahweh a narugit dagiti kapanunotan dagiti tattao.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Nagasat ti tao a suroam, O Yahweh, ti sursuroam kadagiti lintegmo.
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
Ikkam isuna ti inana iti tiempo ti riribuk inggana a makali ti abut a maipaay iti nadangkes.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Ta saan a baybay-an ni Yahweh dagiti tattaona wenno panawan dagiti tawidna.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Ta rumingbawto ti hustisia; ket surotento amin daytoy dagiti nalinteg.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Siasinonto ti tumakder a mangirupir kaniak a maibusor kadagiti managdakdakes? Siasinonto ti mangitakder kaniak a maibusor kadagiti nadangkes?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
No saan a ni Yahweh ti nagbalin a katulongak, nabiitak koman a nakaidda iti lugar ti kinaulimek.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Idi imbagak, “Maikagkaglis ti sakak,” ti kinapudnom ti tulagmo O Yahweh, iti nangingato kaniak.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
No butbutngennak ket ringbawannak dagiti pakariribukak, paragsakennak ti panangliwliwam.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Mabalin kadi a makikadua kenka dagiti dakes nga agtuturay, dagiti agar-aramid iti nakillo a paglintegan?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Agmaymaysada nga agpanggep a mangpapatay kadagiti nalinteg, ken dusaenda dagiti awan ti basolna iti ipapatay.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Ngem ni Yahweh ti nagbalin a nangato a torek salaknibko, ken ti Diosko ti nagbalin a dakkel a bato a pagkamangak.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Iyegna kadakuada dagiti nagkuranganda, ket ikisapna ida gapu iti kinadakesda. Ikisap ida ni Yahweh a Diostayo.

< Zabura 94 >