< Zabura 94 >
1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Du Gott der Rache, o HERR, du Gott der Rache, erscheine!
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Erhebe dich, Richter der Erde, vergilt den Stolzen nach ihrem Tun!
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Wie lange noch sollen die Gottlosen, HERR, wie lange noch sollen die Gottlosen jubeln,
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
sollen sie geifern und trotzige Reden führen, alle Übeltäter stolz sich brüsten?
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Dein Volk, o HERR, zertreten sie und bedrücken dein Erbe;
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
sie erwürgen Witwe und Fremdling und morden die Waisen
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
und sagen dabei: »Nicht sieht es der HERR« oder: »Nicht merkt es der Gott Jakobs.«
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Nehmt Verstand an, ihr Unvernünftigen im Volk, und ihr Toren: wann wollt ihr Einsicht gewinnen?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Der das Ohr gepflanzt, der sollte nicht hören? Der das Auge gebildet, der sollte nicht sehn?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Der die Völker erzieht, der sollte nicht strafen, er, der die Menschen Erkenntnis lehrt?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Der HERR kennt wohl die Gedanken der Menschen, daß nur ein Hauch sie sind.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Wohl dem Manne, den du, HERR, in Zucht nimmst, und den du aus deinem Gesetz belehrst,
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
damit er sich Ruhe verschaffe vor Unglückstagen, bis dem Frevler die Grube man gräbt!
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Denn der HERR wird sein Volk nicht verstoßen und sein Erbe nicht verlassen;
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
denn Recht muß doch Recht bleiben, und ihm werden alle redlich Gesinnten sich anschließen.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Wer leistet mir Beistand gegen die Bösen? Wer tritt für mich ein gegen die Übeltäter?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Wäre der HERR nicht mein Helfer gewesen, so wohnte meine Seele wohl schon im stillen Land.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Sooft ich dachte: »Mein Fuß will wanken«, hat deine Gnade, HERR, mich immer gestützt;
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
bei der Menge meiner Sorgen in meiner Brust haben deine Tröstungen mir das Herz erquickt.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Sollte verbündet dir sein der Richterstuhl des Unheils, der Verderben schafft durch Gesetzesverdrehung?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Sie tun sich ja zusammen gegen das Leben des Gerechten und verurteilen unschuldig Blut.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Doch der HERR ist mir zur festen Burg geworden, mein Gott zu meinem Zufluchtsfelsen;
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
er läßt ihren Frevel auf sie selber fallen und wird sie ob ihrer Bosheit vertilgen: ja vertilgen wird sie der HERR, unser Gott.