< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
Herr! Als der Rache Gott, als Gott der Rache zeige Dich!
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Erhebe Dich als Erdenrichter! Vergilt den Stolzen nach Verdienst!
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Wie lange sollen Frevler, Herr, wie lange sollen Frevler noch frohlocken
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
und geifernd so Vermessenes reden und alle Übeltäter so sich brüsten
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Sie treten, Herr, Dein Volk. Die ewig Deinen quälen sie,
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
erwürgen Fremdlinge und Witwen und morden Waisen, sprechend:
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
"Der Herr sieht's nicht; nicht merkt es Jakobs Gott."
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Ihr Albernen im Volke werdet klug! Ihr Törichten! Wann wollt ihr das begreifen?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Nicht hören sollte, der das Ohr erschafft? Nicht sehen, der das Auge hat gebildet?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Nicht strafen sollte, der die Heidenvölker züchtigt? Er, der den Menschen Einsicht schenkt?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Die menschlichen Gedanken kennt der Herr, wie sie so eitel sind. -
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Dem Manne Heil, den Du erziehst, o Herr, aus Deiner Lehre ihn belehrst,
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
ihn ob des Bösen Glück beruhigend, bis daß gegraben ist die Grube für den Frevler:
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
"Der Herr verstößt sein Volk nicht ganz, verläßt die ewig Seinen nicht.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Noch immer sitzt er zu Gericht; ihm fallen alle frommen Herzen zu."
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Wer steht mir gegen Bösewichter bei? Wer tritt für mich den Übles Tuenden entgegen?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Wenn nicht der Herr mein Beistand wäre, dann läge meine Seele bald im Reich der Stille.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Obschon ich wähnte, daß mein Fuß gewankt, so hält mich dennoch Deine Gnade aufrecht, Herr.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Und streiten sich in meinem Innern die Gedanken, so labt an Deinen Tröstungen sich meine Seele.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Hat schon des Unrechts Stuhl der aufgestellt, der Unheil dem Gesetz bereitet?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Sie klagen fromme Seelen an; unschuldig Blut verdammen sie. -
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Doch eine Burg sei mir der Herr, mein Gott, mein Zufluchtsfels!
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Er lohne ihnen auch ihr Unrecht; er tilge sie in ihrer Bosheit! Der Herr vertilge sie, er, unser Gott.

< Zabura 94 >