< Zabura 94 >
1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
God of vengeance — Jehovah! God of vengeance, shine forth.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Be lifted up, O Judge of the earth, Send back a recompence on the proud.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Till when [do] the wicked, O Jehovah? Till when do the wicked exult?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
They utter — they speak an old saw, All working iniquity do boast themselves.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Thy people, O Jehovah, they bruise, And Thine inheritance they afflict.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Widow and sojourner they slay, And fatherless ones they murder.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
And they say, 'Jehovah doth not see, And the God of Jacob doth not consider.'
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Consider, ye brutish among the people, And ye foolish, when do ye act wisely?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
He who planteth the ear doth He not hear? He who formeth the eye doth He not see?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
He who is instructing nations, Doth He not reprove? He who is teaching man knowledge [is] Jehovah.
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
He knoweth the thoughts of man, that they [are] vanity.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
O the happiness of the man Whom Thou instructest, O Jah, And out of Thy law teachest him,
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
To give rest to him from days of evil, While a pit is digged for the wicked.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
For Jehovah leaveth not His people, And His inheritance forsaketh not.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
For to righteousness judgment turneth back, And after it all the upright of heart,
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Who riseth up for me with evil doers? Who stationeth himself for me with workers of iniquity?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Unless Jehovah [were] a help to me, My soul had almost inhabited silence.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
If I have said, 'My foot hath slipped,' Thy kindness, O Jehovah, supporteth me.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
In the abundance of my thoughts within me, Thy comforts delight my soul.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Is a throne of mischief joined [with] Thee? A framer of perverseness by statute?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
They decree against the soul of the righteous, And innocent blood declare wicked.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
And Jehovah is for a high place to me, And my God [is] for a rock — my refuge,
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
And turneth back on them their iniquity, And in their wickedness cutteth them off; Jehovah our God doth cut them off!