< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
O GOD of avenging—Yahweh, GOD of avenging, shine forth:
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Lift up thyself, O judge of the earth, Render a recompense unto the proud.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
How long shall the lawless, O Yahweh, How long shall the lawless exult?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
They pour forth [words], they speak arrogantly, All the workers of iniquity, do boast:
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Thy people, O Yahweh, they will crush, And, thine inheritance, tread down;
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
The widow and sojourner, they will slay, And, the fatherless, murder.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Yet have they said—Yah, doth not see, The God of Jacob, doth not understand.
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Understand, ye brutish among the people, And, ye dullards, when will ye show discretion?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
He that planteth the ear, shall he not hear? Or, that fashioneth the eye, shall he not have power to see?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
He that correcteth nations, shall he not reprove? He that teacheth man knowledge!
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Yahweh, knoweth the plans of men, That, they, are a breath!
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
How happy the man whom thou correctest, O Yah! And whom, out of thy law, thou instructest!
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
That thou mayest give him rest from the days of misfortune, Until there be digged—for the lawless one—a pit.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
For Yahweh, will not abandon, his people, And, his inheritance, will he not forsake;
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
For, unto righteousness, shall the judicial sentence return, Then shall follow it—all the upright in heart.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Who will rise up for me, against the evil-doers? Who will make a stand for me, against the workers of iniquity?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
If, Yahweh, had not been a help to me, Soon had sunk into silence—my soul!
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
If I say, My foot, hath slipped, Thy lovingkindness, O Yahweh, supporteth me.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
In the multitude of my cares within me, Thy consolations, delight my soul.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Shall the throne that inflicteth ruin, have fellowship with thee, That frameth oppression, by statute?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
They make an attack on the life of the righteous one, —And, innocent blood, they condemn.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
But, Yahweh, hath become for me a high tower, And my God, my rock of refuge.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Thus hath he brought back on them their iniquity, And, by their own wickedness, will he destroy them, Destroy them, will Yahweh our God.

< Zabura 94 >