< Zabura 94 >
1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
The Lord is a God of vengeance! God of vengeance, shine out!
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Stand up, judge of the earth, and pay back those who are proud what they deserve.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
How long, Lord? How long will the wicked celebrate in triumph?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
How long will you let them pour out their arrogant words? How long will these evil people go on boasting?
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Lord, they crush your people; they oppress those you call your own.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
They kill widows and foreigners; they murder orphans.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
They say, “The Lord can't see what we're doing. Israel's God doesn't pay any attention to us.”
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Take another look, you stupid people! Fools—when will you ever get the point?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Do you think the creator of the ear can't hear? Do you think the maker of the eye can't see?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Do you think that the one who punishes nations won't punish you too? Do you think that the one who teaches human beings knowledge doesn't know anything?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
The Lord knows the thoughts of human beings—he knows they are pointless.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Those you discipline are happy, Lord; those you teach from your Law.
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
You give them peace in days of trouble, until a pit is dug to trap the wicked.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
For the Lord will not give up on his people; he will not abandon his own.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Justice will once again be based on what is right; those who are sincere will support it.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Who came to my defense against the wicked; who stood up for me against those who do evil?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
If the Lord hadn't helped me, I would have soon gone down into the silence of the grave.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
I shouted out, “My foot's slipping!” and your trustworthy love, Lord, kept me from falling.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
When my mind was full of worries, you comforted me and encouraged me.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Can unjust judges really be on your side, Lord, when their corrupt use of the law causes misery?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
They work together to destroy good people; they condemn those who are innocent to death.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
But the Lord protects me like a fortress; my God is the rock that keeps me safe.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
He will turn the wickedness of evil people back upon them; he will destroy them because of their sins; the Lord our God will destroy them.