< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
The Lord is the God to whom revenge belongeth: the God of revenge hath acted freely.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Lift up thyself, thou that judgest the earth: render a reward to the proud.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
How long shall sinners, O Lord: how long shall sinners glory?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Shall they utter, and speak iniquity: shall all speak who work injustice?
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Thy people, O Lord, they have brought low: and they have afflicted thy inheritance.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
They have slain the widow and the stranger: and they have murdered the fatherless.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
And they have said: The Lord shall not see: neither shall the God of Jacob understand.
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Understand, ye senseless among the people: and, you fools, be wise at last.
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
He that planted the ear, shall he not hear? or he that formed the eye, doth he not consider?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
He that chastiseth nations, shall he not rebuke: he that teacheth man knowledge?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
The Lord knoweth the thoughts of men, that they are vain.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Blessed is the man whom thou shalt instruct, O Lord: and shalt teach him out of thy law.
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
That thou mayst give him rest from the evil days: till a pit be dug for the wicked.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
For the Lord will not cast off his people: neither will he forsake his own inheritance.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Until justice be turned into judgment: and they that are near it are all the upright in heart.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Who shall rise up for me against the evildoers? or who shall stand with me against the workers of iniquity?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Unless the Lord had been my helper, my soul had almost dwelt in hell. (questioned)
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
If I said: My foot is moved: thy mercy, O Lord, assisted me.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
According to the multitude of my sorrows in my heart, thy comforts have given joy to my soul.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Doth the seat of iniquity stick to thee, who framest labour in commandment?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
They will hunt after the soul of the just, and will condemn innocent blood.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
But the Lord is my refuge: and my God the help of my hope.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
And he will render them their iniquity: and in their malice he will destroy them: the Lord our God will destroy them.

< Zabura 94 >