< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
A Psalm of David himself. The Fourth Sabbath. The Lord is the God of retribution. The God of retribution acts in order to deliver.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Lift yourself up, for you judge the earth. Repay the arrogant with retribution.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
How long will sinners, O Lord, how long will sinners glory?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
How long will they utter and speak iniquity? How long will all who work injustice speak out?
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
They have humiliated your people, O Lord, and they have harassed your inheritance.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
They have executed the widow and the new arrival, and they have slaughtered the orphan.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
And they have said, “The Lord will not see, nor will the God of Jacob understand.”
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Understand, you senseless ones among the people. And be wise at last, you foolish ones.
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
He who formed the ear, will he not hear? And he who forged the eye, does he not look closely?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
He who chastises nations, he who teaches man knowledge, will he not rebuke?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
The Lord knows the thoughts of men: that these are in vain.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Blessed is the man whom you will instruct, O Lord. And you will teach him from your law.
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
So may you soothe him from the evil days, until a pit may be dug for sinners.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
For the Lord will not drive away his people, and he will not abandon his inheritance,
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
even until the time when justice is being converted into judgment, and when those who are close to justice are all those who are upright of heart.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Who will rise up with me against the malignant? Or who will stand with me against the workers of iniquity?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Except that the Lord assisted me, my soul almost would have dwelt in Hell. (questioned)
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
If ever I said, “My foot is slipping,” then your mercy, O Lord, assisted me.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
According to the multitude of my sorrows in my heart, your consolations have given joy to my soul.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Does the seat of iniquity adhere to you, you who contrive hardship within a commandment?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
They will hunt down the soul of the just, and they will condemn innocent blood.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
And the Lord has been made into a refuge for me, and my God into the assistance of my hope.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
And he will repay them their iniquity, and he will destroy them in their malice. The Lord our God will utterly destroy them.

< Zabura 94 >