< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
O God, in whose hands is punishment, O God of punishment, let your shining face be seen.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Be lifted up, O judge of the earth; let their reward come to the men of pride.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
How long will sinners, O Lord, how long will sinners have joy over us?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Words of pride come from their lips; all the workers of evil say great things of themselves.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Your people are crushed by them, O Lord, your heritage is troubled,
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
They put to death the widow and the guest, they take the lives of children who have no father;
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
And they say, Jah will not see it, the God of Jacob will not give thought to it.
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Give your mind to my words, you who are without wisdom among the people; you foolish men, when will you be wise?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Has he by whom your ears were planted no hearing? or is he blind by whom your eyes were formed?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
He who is the judge of the nations, will he not give men the reward of their acts, even he who gives knowledge to man?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
The Lord has knowledge of the thoughts of man, for they are only a breath.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Happy is the man who is guided by you, O Jah, and to whom you give teaching out of your law;
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
So that you may give him rest from the days of evil, till a hole is made ready for the destruction of the sinners.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
The Lord will not give up his people, or take away his support from his heritage;
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
But decisions will again be made in righteousness; and they will be kept by all whose hearts are true.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Who will give me help against the sinners? and who will be my support against the workers of evil?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
If the Lord had not been my helper, my soul would quickly have gone down into death.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
If I say, My foot is slipping; your mercy, O Lord, is my support.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Among all my troubled thoughts, your comforts are the delight of my soul.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
What part with you has the seat of sin, which makes evil into a law?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
They are banded together against the soul of the upright, to give decisions against those who have done no wrong.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
But the Lord is my safe resting-place; my God is the Rock where I am safe.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
And he has made their evil designs come back on themselves, cutting them off in their sin; the Lord our God will put an end to them.

< Zabura 94 >