< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
O LORD, God of vengeance, O God of vengeance, shine forth.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Rise up, O Judge of the earth; render a reward to the proud.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
How long will the wicked, O LORD, how long will the wicked exult?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
They pour out arrogant words; all workers of iniquity boast.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
They crush Your people, O LORD; they oppress Your heritage.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
They kill the widow and the foreigner; they murder the fatherless.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
They say, “The LORD does not see; the God of Jacob pays no heed.”
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Take notice, O senseless among the people! O fools, when will you be wise?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
He who affixed the ear, can He not hear? He who formed the eye, can He not see?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
He who admonishes the nations, does He not discipline? He who teaches man, does He lack knowledge?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
The LORD knows the thoughts of man, that they are futile.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Blessed is the man You discipline, O LORD, and teach from Your law,
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
to grant him relief from days of trouble, until a pit is dug for the wicked.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
For the LORD will not forsake His people; He will never abandon His heritage.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Surely judgment will again be righteous, and all the upright in heart will follow it.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Who will rise up for me against the wicked? Who will stand for me against the workers of iniquity?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Unless the LORD had been my helper, I would soon have dwelt in the abode of silence.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
If I say, “My foot is slipping,” Your loving devotion, O LORD, supports me.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
When anxiety overwhelms me, Your consolation delights my soul.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Can a corrupt throne be Your ally— one devising mischief by decree?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
They band together against the righteous and condemn the innocent to death.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
But the LORD has been my stronghold, and my God is my rock of refuge.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
He will bring upon them their own iniquity and destroy them for their wickedness. The LORD our God will destroy them.

< Zabura 94 >