< Zabura 94 >
1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
上主,您是伸冤的天主,伸冤的天主,求您顯出!
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
審判大地的天主,請您起來!給驕傲人施以應得的禍災!
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
上主,惡人洋洋得意,要到何時?歹徒沾沾自喜,要到何時?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
他們大言不慚,要到何時?作惡的人自誇,要到何時?
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
上主,他們蹂躪您的百姓,他們磨難您的子民,
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
屠殺寡婦與旅客,將孤兒置於死地,
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
他們還說:上主看不見,雅各伯的天主決不管。
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
民間的愚昧者!您們應該知悉,糊塗的人!您們何時才能明白?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
裝置耳朵的,難道自己聽不著?製造眼睛的,難道自己看不到?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
訓戒萬民者,難道自己不懲治?教導人類者,難道自己無知識?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
上主認透人的思念,原來都是虛幻。
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
上主那些受您教訓的人,守您法律者是有福的的人,
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
您叫他在患難獲享安穩,直到給惡人們掘下了陷阱。
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
因為上主不拒絕自己的百姓,上主不遺棄自己的人民。
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
原來公理必歸正義的人士,心地公正的人必追求公理。
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
誰肯奮起替我攻打行兇的人?誰肯站起替我抵抗作惡的人?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
若不是上主扶助我,我的靈魂已歸冥所。
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
我工在想說:我的腳步快要滑倒。上主,您就以您的仁慈來扶助我。
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
憂愁焦思雖然齊集我的心神,您的安慰卻舒暢了我的靈魂。
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
若有人冒充法律,製造苦惱,不義的法庭,豈能與您相好?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
他們殘害義人的性命,判決無辜人的流血刑。
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
然而上主必定作堡壘,我的天主作我避難的磐石。
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
祂必以他們罪過來報復他們;必要用他們的凶惡來消滅他們,上主我們的天主必要消滅他們。