< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
O Pakai, phulaji Pathen, O phula ji Pathen nathutanna dihtah chu loupitah chu hung kilang doh hen.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Hungthou doh in, vainoi thutan pa. Mi kiletsah hochu achanding dol u chansah in!
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Miphalou hohi itih chanpi kipah diuham, ichan gei in em Pakai?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Itih chan kiletsah tah a thu asei diu ham? Hiche migilou hohi itih chanpi kihatsah diu ham?
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Pakai amahon namite asuchip gamtauve. Nangma mite hohi amahon asugenthei’un ahi.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Amahon meithai hole gamdang mi chule chaga ho athat gam un ahi.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Amahon asei un, “Pakai in eive pouve chule, Israel Pathen in anasah poi”.
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Kigel pha kit un, mingol ho! Itihleh tahle nahin hethei diuvem?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Na nakol sempa chu a nangong ham? Namit sempau chu amitcho a ham?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Aman chitin namtinte ana engbol in ahi, nangjong na engbol louding ham? Aman imajouse ahesoh kei in ahi, nangin ipi naboljong ahetsohkei louding ham?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Pakai in mitin lunggel ahesoh kei e, imacha phatchomna neilou ahi ahesoh kei e.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Pakai, nadanthu a nahil hole nasuhdih ho chu iti kipah u hitam?
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
Migilou te kimat nading leiko tong akilai kah sen nangman amaho chu boina akon in lung ol na nape e.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Pakai in amite nungsun ponte; Aman ami deitumte donlou in koi ponte.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Thutanna mun a thudih kimuding chuleh michonpha ho jousen apanhu diu ahi.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Gitlou na akon a koiham eidal ding? Miphalou ho masang a ei din peh ding koi ham?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Pakai in eina kithopi lou hile, keima thina lhankhuh mun a thipchet a ana kicholdo tading kahi.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
“Keima kalhutai” tin kakap jah in, O pakai nami ngailutna longlouchun eiphong dingin ahi.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Keima lungdon na a kadim teng, nami lungmon nachun kinep nale kipa na eipe ji e.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Dandih lou a natong lamkai ho chun Pakai kalang a pangding hi ati ngam nadiu vem?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Themmo nabei ho dou din amaho akipun khom un mona neilou chungah thina chan in athepmo sah uve.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Ahin pakai ka Pathen hi kakisel na songpi kakulpi chu ahi.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Pathen in migiloute achonset nau chu ale thuhding ahi. Achonset nau jeh a asuh gam ding ahi. Pakai I Pathen uvin asuh gam ding u ahi.

< Zabura 94 >