< Zabura 94 >

1 Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
O Jeova, Yuus Jao, ni y inemog iyomo; O Yuus Jao, ni y inemog iyomo, famanuen maesajao ni y minalag.
2 Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
Jatsa jao julo, jago y jues y tano: nae ni y apasñija y mansobetbio.
3 Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
Jeova, asta ngaean y manaelaye, asta ngaean y manaelaye nae ufanmagana?
4 Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
Sija manmefno, sija sumangan sinaguat yan todo y chumochogüe y tinaelaye manbanidoso.
5 Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
Sa sija yumamag ya japedasitos y taotaomo, O Jeova, yan janafanpinite y erensiamo.
6 Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
Sija pumuno y biuda yan taotao juyong, yan japuno y manaetata.
7 Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
Sa ilegñija: Si Jeova ti ujalie, ni si Yuus Jacob ti ufanatituye.
8 Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
Fanatituye, jamyo managuaguat gui taotao: yan jamyo mangaduco, ngaean nae infanmalate?
9 Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
Ya ayo y plumanta y talanga, ada ti ujungog? ya ayo y fumatinas y atadog, ada ti ulie?
10 Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
Ya ayo y cumastiga y taotao sija ada ti ujanafanunas? ayoja y fumanagüe y taotao ni y tiningo?
11 Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
Si Jeova jatungo y jinason y taotao, na sija puro jinaja.
12 Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
Dichoso y taotao ni y unnaregla güe, O Jeova, yan ufanagüe güe ni y tinagomo;
13 kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
Sa jago siña numae gui descanso guinin y jaanin y chinatsaga, asta qui y joyo maguadog para y manaelaye.
14 Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
Sa si Jeova ti janasuja y taotaoña, ni ti udingo y erensiaña.
15 Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
Lao y jinisga utalo guato gui tininas: yan todo y manunas na corason ujadalalag.
16 Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
Jaye malago cajulo para guajo contra y chumochogüe y daño? Jaye malago tumojgue julo para guajo contra y chumochogüe y taelaye?
17 Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
Yanguin si Jeova guinin ti umayudayo, y antijo gusija guinin sumaga gui finatquilo.
18 Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
Anae ileco: Sulong y adengjo: y minaasemo, O Jeova, mumantieneyo.
19 Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
Anae juguaja y manadan jinasoco gui sanjalomjo, y quinensuelamo sija ninasenmagof y antijo.
20 Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
Y tronon tinaelaye uguaja comunion yan jago, ni y fumatinas daño pot y tinago?
21 Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
Sija mandaña contra y anten y manunas, yan ja sentensia y jâgâ y taeisao.
22 Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
Lao si Jeova guinin y leca na torijo: yan Yuusso y achon y guinegüeco.
23 Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.
Ya güiya chumule gui jiloñija y isaoñija, yan ujautut sija gui dañoñijaja; ya si Jeova, ni y Yuusta, umutut sija.

< Zabura 94 >