< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
Salmo: Canción para el día del Sábado. BUENO es alabar á Jehová, y cantar salmos á tu nombre, oh Altísimo;
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
Anunciar por la mañana tu misericordia, y tu verdad en las noches,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
En el decacordio y en el salterio, en tono suave con el arpa.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
Por cuanto me has alegrado, oh Jehová, con tus obras; en las obras de tus manos me gozo.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
¡Cuán grandes son tus obras, oh Jehová! Muy profundos son tus pensamientos.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
El hombre necio no sabe, y el insensato no entiende esto:
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
Que brotan los impíos como la hierba, y florecen todos los que obran iniquidad, para ser destruídos para siempre.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
Mas tú, Jehová, para siempre eres Altísimo.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
Porque he aquí tus enemigos, oh Jehová, porque he aquí, perecerán tus enemigos; serán disipados todos los que obran maldad.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
Empero tú ensalzarás mi cuerno como [el de] unicornio: seré ungido con aceite fresco.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Y mirarán mis ojos sobre mis enemigos: oirán mis oídos de los que se levantaron contra mí, de los malignos.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
El justo florecerá como la palma: crecerá como cedro en el Líbano.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Plantados en la casa de Jehová, en los atrios de nuestro Dios florecerán.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Aun en la vejez fructificarán; estarán vigorosos y verdes;
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
Para anunciar que Jehová mi fortaleza es recto, y que en él no hay injusticia.

< Zabura 92 >