< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
Bueno es alabar a Yavé Y cantar salmos a tu Nombre, oh ʼElyón.
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
Anunciar por la mañana tu misericordia Y tu fidelidad cada noche
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
Con el decacordio y el salterio, Con el armonioso tono del arpa.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
Porque Tú, oh Yavé, me alegraste con lo que hiciste. Por las obras de tus manos doy gritos de júbilo.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
¡Cuán grandes son tus obras, oh Yavé! Tus pensamientos son muy profundos.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
El hombre necio no sabe Y el insensato no entiende esto:
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
Que cuando los perversos brotan como hierba, Y florecen todos los que hacen iniquidad, [Solo sucede] para que sean destruidos eternamente.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
Pero Tú, oh Yavé, eres altísimo para siempre.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
Porque ya veo que tus enemigos, oh Yavé, Ya veo que tus enemigos perecen. Son dispersados todos los obradores de iniquidad.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
Pero Tú aumentarás mi fuerza como la del búfalo. Seré ungido con aceite fresco.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Y mis ojos mirarán por encima de mis enemigos. Mis oídos escucharán Con respecto a los perversos que se levantan contra mí.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
El justo florecerá como la palmera. Crecerá como un cedro en el Líbano.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Plantados en la Casa de Yavé, Florecerán en los patios de nuestro ʼElohim.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Aun en la vejez darán fruto. Estarán llenos de savia y muy verdes
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
Para manifestar que Yavé es recto. Mi Roca es. En Él no hay injusticia.

< Zabura 92 >