< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
Un salmo. Una canción para el día Sábado. Cuán bueno es agradecer al Señor, cantarte alabanzas a ti, Altísimo,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
hablar de tu gran amor por las mañanas, y de tu fidelidad por las noches,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
a la música de un arpa de diez cuerdas y de la lira.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
Oh, Señor, ¡Me has hecho tan feliz con todas las cosas que has hecho por mí! Canto de alegría por lo que has hecho.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
Señor, ¡Lo que haces es maravilloso; tus pensamientos son muy profundos!
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
Solo la gente tonta e insensible no conoce ni entiende esto:
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
aunque la gente mala crezca tan rápido como la grama, e incluso aunque florezcan, ¡Ellos serán destruidos para siempre!
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
Pero tú, Señor, gobernarás para siempre.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
Tus enemigos, Señor, tus enemigos morirán; ¡Todo el que haga el mal morirá!
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
Pero tú me has hecho tan fuerte como un toro salvaje; me has ungido con el mejor aceite.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Mis ojos se placen al ver a mis enemigos derrotados; mis oído han escuchado sobre la caída de aquellos que me atacaban.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
Los que viven con rectitud florecerán como árbol de palma; crecerán tan alto como un cedro en el Líbano.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Son plantados en la casa del Señor; y prosperarán en los atrios de nuestros Dios.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Incluso cuando envejezcan seguirán produciendo fruto, permaneciendo frescos y verdes.
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
Declararán, “¡El Señor hace el bien! ¡Él es mi roca! ¡No hay nada malo en él!”

< Zabura 92 >