< Zabura 92 >
1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
Lijepo je hvaliti Gospoda, i pjevati imenu tvojemu, višnji,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
Javljati jutrom milost tvoju, i istinu tvoju noæu,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
Uz deset žica i uz psaltir, i uz jasne gusle!
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
Jer si me razveselio, Gospode, djelima svojim, s djela ruku tvojih radujem se.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
Kako su velika djela tvoja, Gospode! Veoma su duboke pomisli tvoje.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
Bezumnik ne zna, i neznalica ne razumije toga.
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
Kad bezbožnici nièu kao trava i cvjetaju svi koji èine bezakonje, to biva zato da bi se istrijebili dovijeka.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
A ti si, Gospode, visok uvijek.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
Jer evo neprijatelji tvoji, Gospode, jer evo neprijatelji tvoji ginu, i rasipaju se svi koji èine bezakonje;
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
A moj rog ti uzvišuješ kao rog u jednoroga, ja sam pomazan novijem uljem.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
I oko moje vidi neprijatelje moje, i o bezakonicima, koji ustaju na mene, slušaju uši moje.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
Pravednik se zeleni kao finik, kao kedar na Livanu uzvišuje se.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Koji su zasaðeni u domu Gospodnjem, zelene se u dvorovima Boga našega;
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Rodni su i u starosti, jedri i zeleni,
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
Javljajuæi da je pravedan Gospod, braniè moj, i da nema u njemu nepravde.