< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
Psaume. Cantique pour le jour du Sabbat. Il est beau de rendre grâce à l’Eternel, de chanter en l’honneur de ton nom, ô Dieu suprême,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
d’annoncer, dès le matin, ta bonté, et ta bienveillance pendant les nuits,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
avec la lyre à dix cordes et le luth, aux sons harmonieux de la harpe.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
Car tu me combles de joie, ô Eternel, par tes hauts faits; je veux célébrer les œuvres de tes mains.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
Qu’elles sont grandes tes œuvres, ô Eternel, infiniment profondes tes pensées!
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
L’Homme dépourvu de sens ne peut savoir, le sot ne peut s’en rendre compte:
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
si les méchants croissent comme l’herbe, et que fleurissent tous les artisans d’iniquité, c’est pour encourir une ruine irréparable.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
Mais toi, Seigneur, tu es éternellement sublime;
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
car voilà que tes ennemis, ô Eternel, voilà que tes ennemis succombent, que se disloquent tous les ouvriers du mal,
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
tandis que tu grandis ma force comme celle du reêm, et que ma décrépitude reverdit au contact de l’huile.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Avec satisfaction, mes yeux contemplent mes ennemis, mes oreilles entendent les malfaiteurs se dresser contre moi.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
Le juste fleurit comme le palmier; comme le cèdre du Liban, il est élancé.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Plantés dans la maison de l’Eternel, ils sont florissants dans les parvis de notre Dieu.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Jusque dans la haute vieillesse, ils donnent des fruits, ils sont pleins de sève et de verdeur,
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
prêts à proclamer que l’Eternel est droit, qu’il est mon rocher, inaccessible à l’injustice.

< Zabura 92 >