< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
Psaume. Cantique pour le jour du sabbat. Il est bon de célébrer l’Éternel, et de chanter des cantiques à [la gloire de] ton nom, ô Très-haut!
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
D’annoncer le matin ta bonté, et ta fidélité dans les nuits,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
Sur l’instrument à dix cordes, et sur le luth, et sur le higgaïon avec la harpe.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
Car, ô Éternel! tu m’as réjoui par tes actes; je chanterai de joie à cause des œuvres de tes mains.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
Éternel! que tes œuvres sont grandes! Tes pensées sont très profondes:
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
L’homme stupide ne le connaît pas, et l’insensé ne le comprend pas.
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
Quand les méchants poussent comme l’herbe et que tous les ouvriers d’iniquité fleurissent, c’est pour être détruits à perpétuité.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
Mais toi, Éternel! tu es haut élevé pour toujours.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
Car voici, tes ennemis, ô Éternel! car voici, tes ennemis périront, tous les ouvriers d’iniquité seront dispersés.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
Mais tu élèveras ma corne comme celle du buffle; je serai oint d’une huile fraîche.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Et mon œil verra [son plaisir] en mes ennemis, et mes oreilles se repaîtront du sort des méchants qui s’élèvent contre moi.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
Le juste poussera comme le palmier, il croîtra comme le cèdre dans le Liban.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Ceux qui sont plantés dans la maison de l’Éternel fleuriront dans les parvis de notre Dieu.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Ils porteront des fruits encore dans la blanche vieillesse, ils seront pleins de sève, et verdoyants,
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
Afin d’annoncer que l’Éternel est droit. Il est mon rocher, et il n’y a point d’injustice en lui.

< Zabura 92 >