< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
Un psaume. Un chant pour le jour du sabbat. C'est une bonne chose que de rendre grâce à Yahvé, pour chanter les louanges de ton nom, le Très-Haut,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
pour proclamer ta bonté dès le matin, et votre fidélité chaque nuit,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
avec le luth à dix cordes, avec la harpe, et avec la mélodie de la lyre.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
Car toi, Yahvé, tu m'as réjoui par ton œuvre. Je triompherai dans les œuvres de tes mains.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
Que tes œuvres sont grandes, Yahvé! Vos pensées sont très profondes.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
Un homme insensé ne sait pas, Un imbécile ne le comprend pas non plus:
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
Les méchants poussent comme l'herbe, et tous les malfaiteurs prospèrent, ils seront détruits à jamais.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
Mais toi, Yahvé, tu es en haut pour toujours.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
Car voici tes ennemis, Yahvé, car voici que vos ennemis vont périr. Tous les malfaiteurs seront dispersés.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
Mais tu as élevé ma corne comme celle du bœuf sauvage. Je suis oint d'une huile fraîche.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Mon œil a aussi vu mes ennemis. Mes oreilles ont entendu parler des méchants ennemis qui se dressent contre moi.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
Le juste fleurira comme le palmier. Il grandira comme un cèdre au Liban.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Ils sont plantés dans la maison de l'Éternel. Ils s'épanouiront dans les cours de notre Dieu.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Ils produiront encore des fruits dans leur vieillesse. Ils seront pleins de sève et de vert,
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
pour montrer que Yahvé est droit. Il est mon rocher, et il n'y a pas d'injustice en lui.

< Zabura 92 >