< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
A Psalm. — A Song for the sabbath-day. Good to give thanks to Jehovah, And to sing praises to Thy name, O Most High,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
To declare in the morning Thy kindness, And Thy faithfulness in the nights.
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
On ten strings and on psaltery, On (higgaion) with harp.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
For Thou hast caused me to rejoice, O Jehovah, in Thy work, Concerning the works of Thy hands I sing.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
How great have been Thy works, O Jehovah, Very deep have been Thy thoughts.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
A brutish man doth not know, And a fool understandeth not this; —
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
When the wicked flourish as a herb, And blossom do all workers of iniquity — For their being destroyed for ever and ever!
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
And Thou [art] high to the age, O Jehovah.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
For, lo, Thine enemies, O Jehovah, For, lo, Thine enemies, do perish, Separate themselves do all workers of iniquity.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
And Thou exaltest as a reem my horn, I have been anointed with fresh oil.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
And mine eye looketh on mine enemies, Of those rising up against me, The evil doers, do mine ears hear.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
The righteous as a palm-tree flourisheth, As a cedar in Lebanon he groweth.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Those planted in the house of Jehovah, In the courts of our God do flourish.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Still they bring forth in old age, Fat and flourishing are they,
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
To declare that upright [is] Jehovah my rock, And there is no perverseness in Him!

< Zabura 92 >