< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
A psalm, a song for the Sabbath day. It is a good thing to give thanks to Yahweh and to sing praises to your name, Most High,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
to proclaim your covenant faithfulness in the morning and your truthfulness every night,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
with a harp of ten strings and with the melody of the lyre.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
For you, Yahweh, have made me glad through your deeds. I will sing for joy because of the deeds of your hands.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
How great are your deeds, Yahweh! Your thoughts are very deep.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
A brutish person does not know, nor does a fool understand this:
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
When the wicked sprout like the grass, and even when all the evildoers thrive, still they are doomed to eternal destruction.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
But you, Yahweh, will reign forever.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
Indeed, look at your enemies, Yahweh! Indeed, look at your enemies. They will perish! All those who do evil will be scattered.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
You have lifted up my horn like the horn of the wild ox; I am anointed with fresh oil.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
My eyes have seen the downfall of my enemies; my ears have heard of the doom of my evil foes.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
The righteous will flourish like the palm tree; they will grow like a cedar in Lebanon.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
They are planted in the house of Yahweh; they flourish in the courts of our God.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
They bear fruit even when they are old; they stay fresh and green,
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
to proclaim that Yahweh is just. He is my rock, and there is no unrighteousness in him.

< Zabura 92 >