< Zabura 92 >

1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
A psalm. A song; for the sabbath day. It is good to give thanks to the Lord, to sing praise to your name, O Most High,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
to declare your love in the morning, and your faithfulness in the night,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
with voice and a ten-stringed harp, with music that throbs on the lyre.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
For you make me glad by your deeds, Lord, at the work of your hands I will ring out my joy.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
How great are your works, O Lord; how deep are your thoughts!
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
The insensitive cannot know, nor can a fool understand,
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
that, though the wicked flourish like grass, and evildoers all blossom, they will perish forever.
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
But you are exalted forever.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
For see! Your enemies, Lord For see! Your enemies perish, all evildoers are scattered.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
But you lift me to honor, and anoint me afresh with oil.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
My eyes will feast on my foes, and my ears will hear of the doom of the wicked.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
The righteous will sprout like the palm, will grow like a cedar of Lebanon.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
In the house of the Lord are they planted, in the courts of our God they will sprout.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
They will still bear fruit in old age, all sappy and fresh will they be
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
So they proclaim the Lord to be just, my rock, in whom is no wrong.

< Zabura 92 >