< Zabura 92 >
1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
A PSALM. A SONG FOR THE SABBATH DAY. [It is] good to give thanks to YHWH, And to sing praises to Your Name, O Most High,
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
To declare Your kindness in the morning, And Your faithfulness in the nights.
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
On ten strings and on stringed instrument, On (higgaion) with harp.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
For You have caused me to rejoice, O YHWH, in Your work, I sing concerning the works of Your hands.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
How great Your works have been, O YHWH, Your thoughts have been very deep.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
A brutish man does not know, And a fool does not understand this—
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
When the wicked flourish as an herb, And all workers of iniquity blossom—For their being destroyed forever and ever!
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
And You [are] high for all time, O YHWH.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
For behold, Your enemies, O YHWH, For behold, Your enemies perish, All workers of iniquity separate themselves.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
And You exalt my horn as a wild ox, I have been anointed with fresh oil.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
And my eye looks on my enemies, Of those rising up against me, The evildoers, my ears hear.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
The righteous flourish as a palm-tree, He grows as a cedar in Lebanon.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Those planted in the house of YHWH, In the courts of our God, flourish.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
Still they bring forth in old age, They are fat and flourishing,
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
To declare that YHWH my Rock [is] upright, And there is no perverseness in Him!