< Zabura 92 >
1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
A Psalm [or] Song for the sabbath day. [It is a] good [thing] to give thanks unto the LORD, and to sing praises unto thy name, O most High:
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
To shew forth thy lovingkindness in the morning, and thy faithfulness every night,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
Upon an instrument of ten strings, and upon the psaltery; upon the harp with a solemn sound.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
For thou, LORD, hast made me glad through thy work: I will triumph in the works of thy hands.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
O LORD, how great are thy works! [and] thy thoughts are very deep.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
A brutish man knoweth not; neither doth a fool understand this.
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
When the wicked spring as the grass, and when all the workers of iniquity do flourish; [it is] that they shall be destroyed for ever:
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
But thou, LORD, [art most] high for evermore.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
For, lo, thine enemies, O LORD, for, lo, thine enemies shall perish; all the workers of iniquity shall be scattered.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
But my horn shalt thou exalt like [the horn of] an unicorn: I shall be anointed with fresh oil.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Mine eye also shall see [my desire] on mine enemies, [and] mine ears shall hear [my desire] of the wicked that rise up against me.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
The righteous shall flourish like the palm tree: he shall grow like a cedar in Lebanon.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Those that be planted in the house of the LORD shall flourish in the courts of our God.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
They shall still bring forth fruit in old age; they shall be fat and flourishing;
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
To shew that the LORD [is] upright: [he is] my rock, and [there is] no unrighteousness in him.