< Zabura 92 >
1 Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
IT IS A GOOD THING TO GIVE THANKS UNTO THE LORD, AND TO SING PRAISES UNTO Your NAME, O MOST HIGH:
2 don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
To show forth your loving kindness in the morning, and your faithfulness every night,
3 da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
Upon an instrument of ten strings, and upon the psaltery; upon the harp with a solemn sound.
4 Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
For you, LORD, have made me glad through your work: I will triumph in the works of your hands.
5 Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
O LORD, how great are your works! and your thoughts are very deep.
6 Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
A brutish man knows not; neither does a fool understand this.
7 cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
When the wicked spring as the grass, and when all the workers of iniquity do flourish; it is that they shall be destroyed for ever:
8 Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
But you, LORD, are most high for evermore.
9 Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
For, lo, your enemies, O LORD, for, lo, your enemies shall perish; all the workers of iniquity shall be scattered.
10 Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
But my horn shall you exalt like the horn of an unicorn (ox): I shall be anointed with fresh oil.
11 Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
Mine eye also shall see my desire on mine enemies, and mine ears shall hear my desire of the wicked that rise up against me.
12 Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
The righteous shall flourish like the palm tree: he shall grow like a cedar in Lebanon.
13 da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
Those that be planted in the house of the LORD shall flourish in the courts of our God.
14 Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
They shall still bring forth fruit in old age; they shall be fat and flourishing;
15 suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”
To show that the LORD is upright: he is my rock, and there is no unrighteousness in him.